Tsoho Ya Roki Malamin Addini Kan Ya Aura Masa Mata Ta Biyar, Bidiyon Ya Haddasa Cece-kuce


  Wani dattijo wanda ya je bauta a cocin Fasto Ezekiel

Odero ya bar malamin addinin cikin mamaki bayan ya

gabatar da bukatarsa

– Tsohon ya bukaci Ezekiel da ya taimaka masa da matar

aure, yana mai cewa mata biyu da ya fara aura sun bar shi

sannan ya sake auren wasu biyu amma suka mutu

– Mutumin wanda ke zaune a yanzu babu aure ya ce yana

neman dattijuwa yar shekaru 52 zuwa 59 kuma wacce ta

daina haihuwa don so yake ya hole a karshen rayuwarsa

Kenya - Wani dattijo mutumin kasar Kenya ya yiwa cocin

Fasto Ezekiel Odero da Mavueni, Kilifi tsinke sannan ya

bukaci malamin addinin da ya yi masa addu'an samun

matar aure.

Tsoho Ya Bige Da Rokon Malamin Addini Kan Ya Aura

Masa Mata Ta Biyar, Bidiyon Ya Haddasa Cece-kuce Hoto:

New Life Church.

Fasto Ezekiel ya cika da mamaki bayan mutumin ya roke

shi mata

Mutumin wanda kansa ke cike da furfura ya ba Ezekiel

labarin yadda ya auri mata hudu a baya amma a yanzu ya

saura babu mace.

Budurwa Mai Tallan Tuwo a Najeriya Ta tsallake, Ta Tare

Da Mijinta a Turai, Sun Bar Jama'a Baki Bude

Dattijon ya bayyana cewa matasan biyu da ya fara aura sun

rabu da shi sannan ya sake auren wasu biyu amma su

dukka suka mutu kuma yanzo yana neman wacce za su yi

rayuwa tare.

Faston wanda ke auren Fasto Sarah ya tambaye shi : " Shin

kana son sabuwar mata?"

Sai dattijon ya amsa da:

"Eh, ina son sabuwar mata amma bana son wacce za

ta haihu. Ina son dattijuwa tsakanin shekaru 52 zuwa

59. Wacce ba za ta zo da tarin bukatu ba don yarana

su iya daukar dawainiyarmu mu biyu."

Ya kara da cewar:

"Ba na son samun karin 'ya'ya saboda bani da sauran

fili da zan basu kuma ba zan iya daukar dawainiyar

makarantarsu ba. Kawai ina son matar da zan iya

more rayuwa tare da ita cikin farin ciki."

Himma Ba Ta Ga Rago: Gurgu Ya Mayar Da Kekensa Ya

Zama Shagon Siyar Da Kaya a Bidiyo

Bukatar da mutumin ya gabatar ya bar Ezekiel da

mabiyansa cikin mamaki.

Da dama sun cika da mamakin bukatar da mutumin ya

gabatar, inda wasu ke cewa zuwa neman shawara da

addu'a a wajen Ezekiel kuskure ne don baya goyon bayan

auren mata da yawa da na masu tazarar shekaru.

Magidanci mai yara 102 na fama da rayuwa

A halin yanzu, Legit.ng ta rahoto a baya cewa wani dattijo

mai shekaru 67, Musa Hasahya, wanda ke zama a Lusaka,

Uganda, ya bayyana cewa yanzu baya so ya sake haihuwa .

Manomin ya yanke shawarar ne bayan ya haifi yara 102 da

jikoki 568 daga mata 12.

Comments

Popular posts from this blog