Tapswap code 14 July....
su ba’, za mu yi nasara
-Tinubu
Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC mai
mulki, Bola Tinubu, a ranar Larabar da ta gabata ya yi
zargin cewa ana shirin yin magudi a babban zaben
kasar.
A ranar 25 ga watan Fabrairu da 11 ga watan Maris ne
za a gudanar da zabukan na tarayya da na jihohi.
Amma yayin da yake jawabi a babban filin wasa na
Moshood Abiola International Stadium, Abeokuta, jihar
Ogun, Tinubu ya ce akwai wasu da ke kokarin ganin ba
a yi zabukan a wadannan rana ba, wato suna son su
kawo cikas ga zabukan.
Tinubu ya ce karancin man fetur da ake fama da shi a
fadin kasar nan da kuma sake fasalin kudin Najeriya
wato Naira na daga cikin shirin yi wa zaben zagon
kasa.
Sai dai ya tabbatar wa magoya bayansa, wadanda
dubbansu suka halarci gangamin, cewa ba za a iya
hana wannan zabe ba ko nasarar sa a zaben ba.
Wannan zabe gwagwarmaya ce, kuma jihadi, za mu
karbi mulki daga hannunsu, ba sa son a yi zabe, amma
ba za mu yarda ba, suna son fakewa da karancin man
fetur don haddasa rikicin ta yadda za a samu. ba za a
yi zabe ba,” in ji Tinubu.
Ko da man fetur ko babu, za mu yi zabe. Ba tare da
man fetur ba, za mu yi zabe. Kun san ni sosai, za mu
yi nasara, za mu karbi ragamar mulki daga hannunsu.
Za mu hadu aii a ranar zabe.
Manyan jiga-jigan APC a jihar duk sun halarci taron
gangamin da suka hada da tsohon gwamnan jihar
Gbenga Daniel, tsohon kakakin majalisar tarayya, Dimeji
Bankole da dai sauran su.
Comments
Post a Comment