Tapswap code 14 July....
shugabannin ƙasashen Afirka da su mayar da hankali
wajen ƙara bunƙasa harkokin noma a nahiyar.
A wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban
ƙasar Femi Adesina ya fitar ya ce shugaba Buhari na
jawabin ne a taron harkokin noma da shugabannin
kasashen Afirka ke halarta a birnin Dakar na ƙasar
Senegal.
Buhari ya yi kira ga takwarorinsa shugabannin ƙasashen
Afirka da su rungumi sabbin tsare-tsaren noma domin
tabbatar da samar da abincin da zai ciyar da nahiyar
har a fitar da shi zuwa ƙasahen ƙetare.
A yayin da duniya ke fuskantar hauhawar farashin kayan
abinci sanadiyyar yaƙin Ukraine, musamman kan alkama
da masara, shugaban na Najeriya ya zayyano wasu
matakan da ya kamata shugabannin Afirka su ɗauka
domin sauya wannan matsala.
'‘Ciyar da Afirka wajibi ne. ‘‘Dole mu tabbatar da
cewa muna ciyar da kanmu a yau da gobe da ma
kuma nan gaba. Abin da za mu fara yi shi ne mu
haɓaka harkokin noma a ƙasashenmu'', in ji Buhari
''Wannan na buƙatar samar wa manoma abubuwan da
suke buƙata kamar ingataccen irin shuka da wadataccen
takin zamani da sabbin dabarun noma''.
‘‘Idan muna son yin nasara dole mu tallafa wa
manomanmu, babu shakka akwai buƙatar taimaka wa
manoma, amma ya kamata mu yi haka cikin gaskiya,
mu cire musu ɗabi'ar neman rance, a maimakon haka
mu tallafa wa manoma''.
‘‘Ya kamata ƙasashen Afirka su ƙara kauɗi a
ɓangaren noma a kasafin kuɗinsu, musamman zuba jari
domin samar da abubuwan da ake buƙata kamar
haɓaka bincike da samar da abubuwan more rayuwa
musamman hanyoyi da noman rani da kuma
makamashi'', in ji Buhari.
Comments
Post a Comment