Mene ne Gaskiya? Da Gaske Bola Tinubu Zai Kara Aure? Yayi Bayan Dalla-Dalla

 – Asiwaju Bola Tinubu ya karyata batun kara aurensa da

ya karade ko ina a yanar gizo, inda ya bayyana yadda suke

zaune lami lafiya gami da more rayuwar aurensu shi da

matarsa

– 'Dan takarar shugaban kasar jam'iyyar APC, ya kara da

cewa, shi bai da niyyar dankaro wa matarsa kishiya, batu

ne kawai na masu son janyo rikici cikin iyalinsa

– Ya kara da cewa, burinsu ba zai taba cika ba, saboda

shi da matarsa a yanzu sun fi mayar da hankali kan

fafutukar yakin neman kuri'un don lashe zaben shugaban

kasa

'Dan takarar shugaban kasar jam'iyyar APC, Asiwaju Bola

Tinubu ya karyata "Wani labarin kanzon kurege" da ke yawo

a yanar gizo cewa zai kara aure, inda ya bayyana yadda

yake jindadin rayuwar aurensa da matarsa, Sanata Oluremi





Bola Tinubu ya Magantu Kan Rade-Rafin Kara Aure da Ake

Yadawa Zai yi. Hoto daga Vanguardngr.news

Mai magana da yawunsa, Tundra Rahman ne ya bayyana

hakan a wata takarda mai taken,:

"Ku Daina Yada Labarin Kanzon Kurege: Asiwaju Bola

Tinubu bai da niyyar kara aure.”

Takarda wacce ta fita daren Lahadi a Abuja .

"Mun ga labaran kanzon kuregen da ke yawo a yanar

gizo na cewa 'dan takarar shugaban kasar jam'iyyar

APC, Asiwaju Bola Tinubu zai kara aure.

"Wannan labarin kanzon kurege ne wanda bai da

tushe.

"Shi Asiwaju na morar aurensa da matarsa, Sanata

Oluremi Tinubu, wacce aka albarkata da 'ya'ya na

kwarai. Bai shirya kara aure ba, Musulma ko Kirista.”

- Kamar yadda takardar ta bayyana daga Ofishin yada

labaran Tinubu.

Kamar yadda takardar ta bayyana:

”Burin wadan da ke yada cewa zai auri musulma ba

kawai don su janyo rikici cikin iyalin Tinubu kadai bane,

sai don su jawo kiyayya tsakanin al'ummar kiristanci.

Shugaban Kasa: Duk Dan Takarar Da Wike Ya Marawa

Baya Ba Zai Ci Zabe Ba, Malamin Addini Ya Yi Gargadi

"Burinsu ba zai cika ba. Hakan ba zai yi tasiri ba."

Takardar ta roki 'yan Najeriya da su yi watsi da labarin

karyar.

"A halin yanzu, Asiwaju ya maida hankalinsa kan

kamfen don lashe zaben shugaban kasa da zai gudana

ranar 25 ga watan Fabrairu, 2023, ko ya dawo wa

jama'a buri, data da tsaro da farincikin Najeriya.

"Sanata Oluremi ita ma tana tsaka da fafutukar nemar

wa mijinta magoya baya. Hankalinsu bazai da


wo ga

abaran kanzon kurege ba,"

Comments

Popular posts from this blog