RIJIYA GABA DUBU LITTAFI NA DAYA(1) part 1



 RIJIYA GABA DUBU

Littafi na daya 1

Na Abdulaziz sani m gini

Typing:- yusuff smært


Part 1📌


_____________________

.

marubucin littafin yace

Saurayin gudu yake iya karfinsa acikin dajin

domin ya

ceci rayuwarsa,

.

yana gudu yana waigen bayansa cikin

tsananin tsoro,amma baya ganin komai kuma

baya

jin sautin komai face na masifaffun karnukan

dake

biye dashi.

.

Su dai wadan nan karnuka sun kai guda saba in

da

doriya kuma sun kasance jibga jibga tamkar ba

karnuka bane kai kace kurayene sabo da

girmansu da

kwarjininsu gami da ban tsoro,musamman aka

kiwata wadan nan karnukan kuma aka basu horo

na

musamman domin suyi gadin babban kurkuku na

birnin Kisra.

.

A tarihin birnin na kisra tunda aka gina kurkukun

tsawon shekaru arba in ba ataba samun fursuna

da

ya taba guduwa daga cikin sa ba sabo da karfin

tsaron da ke cikinsa sai wannan saurayi wanda

ake

kira IMHAL IBN IMZANU,

.

sabo da tsananin karfin

gudun Imhal ne ya baiwa karnukan tazara ta

kimanin

taku sittin amma sabo da nacin karnukan da

mugun

horon da suka samu sai gashi sun fara hango

shi,nan

fa suka kara kaimi,nan fa Imhal ya kara kaimin

gudunsa alokacin da ya waigo ya hango su yaci

gaba

da falfala azababben gudu ta cikin kwazazzabai

da

sarkakiya,

sabo da karfin gudun ma har tashi sama

yake yana tsallake duwatsu da karyayyun

bishiyoyin

da suka fadi kasa

.

Shi dai Imhal gudun kawai yake yi acikin dajin

amma

baisan inda yake dosa ba,sabo da baisan ma a

inda

yake ba bare ma yasan hanyar da ya kamata

yabi, a

duk sanda ya tuno da bakar wahalar da ya sha

kafin

ya sami nasarar guduwa daga kurkukun sai ya

kara

kaimin gudun nasa yana mai ayyanawa a ransa

da dai

a kamasa a raye a mai dashi cikin kurkukun

gwara a

sami gawarsa sabo da azabar da take cikin

kurkukun

ta wuce tunanin mai tunani.

.

Asalin Imhal bin Imzanu mutumin birnin misira ne

kuma shi ba dan kowa bane kuma bai aikata

laifin

komai ba,mahaifinsa wani makiyayi ne mai kiwon

dabbobi a daji,don haka rayuwar Imhal gaba daya

a

cikin daji take,sai dai a karshen kowane sati

ranar

Lahadi sukan shiga cikin gari suyi dan siye-siyen

su

sannan su koma daji inda suka gina bukkarsu.

.

Imhal ya taso da Jarumtaka juriya da iya

farauta,sanan komai yawan dabbobi idan ya tafi

kiwo

dasu yana iya sarrafa su

.

Lokacin da Imhal ya fara girma ya cika shekaru

goma

sha shida ne ya tambayi mahaifinsa tsoho

Imzanu

yace ya kai Abbana me yasa baka taba bani

labarin

mahaifiyata ba?ban santa ba kuma bansan yanda

akayi ta mutu ba kullum sai kace dani kawai

mutuwa

tayi,kayi sani cewa yanzu ni ba yaro bane karami

na

mallaki hankalin kaina yakamata ka sanar dani

gaskiyar al amari,

koda tsoho Imzanu yaji wannan

batu sai hankalinsa ya dugunzuma ainun yayi

shiru

yana mai sunkui da kansa kasa,kawai sai

idanunsa

suka ciko da kwalla hawaye ya fara zubowa kas,

a sannan ne ya dago kai ya dubi Imhal yace

yakai dana

kasani yau ka tambayeni wani sirri wanda dama

nayi

alkawarin bazan sanar dakai ba sai bayan ka

mallaki

hankalinka,don kada hankalinka ya dugunzuma

kwakwalwarka ta kasa daukar al amarin, koda

imzanu

yazo nan a zancensa sai ya sake yin shiru kamar

bazai

iya cewa komai ba,da kyar ya sake dago kai ya

dubi

Imhal muryarsa na rawa yace ka gafarceni yakai

dana

bisa abinda zaka ji daga bakina yanzu domin

zakayi

matukar mamaki kuma zai iya girgiza

ka,maganar

gaskiya ita ce ni ba mahaifinka bane na jini,koda

jin

wannan batu sai zuciyar Imhal ta buga da

karfi,nan

take idanunsa suka kada sukayi jawur,bai san

sanda

hawaye ya zubo masa ba yace yanzu idan ba

kaine

mahifina ba to wanene? Bansan kowa ba a

rayuwata

sai dai kai kadai,

kaine kasan cina da shana tundaga

kuruciyata har izuwa yanzu,me yasa uban nawa

ya

gujeni ya barni a wajanka cikin daji inda babu jin

dadi da tsaro?

.

lallai kuwa ashe babu soyayya tsakani

na da uban nawa tunda bai damu da rayuwata

ba.

Koda Imhal yazo nan a zancensa sai tsoho

imzanu ya zubar

da hawaye sannan yace

Ni kaina bansan waye

mahaifinka ba,ka saurara dakyau kaji labarin da

zan

baka yanzu,

wata kila idan kaji labarin zuciyarka tayi

sanyi ka rungumi kaddara a bisa halin da ka

tsinci

kanka a ciki

....... ..¤¤¤¤¤¤¤

Wata rana da safe na fito kiwo acikin dajin nan

ina

kada dabbobi na sai kawai na hango wasu

mutane

bisa keken doki sanye da bakaken tufafi kuma

sun

rufe fuskokinsu su biyu sun nufi bakin wani katon

rami mai zurfi da fadin gaske,cikin hanzari na

kada

dabbobina izuwa cikin duhuwar bishiyoyi nima na

sami wuri na buya,

dama wadannan mutane basu

ganni ba,ina nan labe cikin duhuwa sai naga

wadannan mutane sun fiddo gawar wata mace

daga

cikin keken dokin sun cillata cikin wannan

ramin,

kawai sai suka shiga cikin keken dokinsu da

sauri suka fice daga cikin dajin gaba daya,sai da

na

tabbatar da cewa sunyi nisa da tafiya kuma babu

alamar cewa zasu dawo sannan na ruga izuwa

bakin

wannan ramin na leka cikinsa kawai sai naga

ashe

wata kyakkyawar mace ce aka yanka ta har a

sannan

jini na bulbulowa daga cikin makogwaronta kuma

tana dauke da tsohon juna biyu,nan take naji na

kamu da tsananin tausayinta,

.

don haka sai na yanke

shawarar na shiga cikin ramin na dauko gawar

wannan mata domin na suturta ta sosai na haka

kabari mai kyau na binne ta,idan ma na barta

acikin

ramin zata rube ne warinta ya dameni tunda

ramin

yana kusa da inda bukkata take,nan fa na fara

tunanin

dabarar da zanyi na iya shiga cikin wanna har

na iya dauko gawar,sai da nayi tunani na tsawon

'yan

dakiku sannan dabara ta fado mini,kawai sai na

ruga

da gudu izuwa cikin bukkata,na dauko igiya mai

tsawo

sannan na dawo bakin ramin,na daura igiyar a

jikin

wata bishiya na wurgata cikin ramin sannan na

kama

igiyar ina binta ina shiga ramin,sannu a hankali

na isa

kasan ramin,koda naje kan gawar na duba ta sai

naga

ashe da ranta bata mutu ba domin numfashinta

na

fita kadan-kadan,cikin gaggawa na sunkuci

wannan

mace na goya ta a bayana na daureta tamau,na

sake

kama igiyar nayi iya kokarina na fito daga cikin

ramin

goye da matar a baya na,hankalina a

dugunzume,sauri nake kawai na jarraba ceto

rayuwarta,ina fita daga cikin ramin na ruga da ita

izuwa cikin bukkata,na shimfide ta a kasa

sannan nayi

sauri na dauko allura da zarin dinke fata na dinke

raunin wuyanta sannan na shafa magani akan

raunin,A sannan ne na kara hancina a dai dai

hancin

matar don naji ko tana yin numfashi,amma sai

naji

shiru alamar babu rai a jikinta,nan fa bakin ciki

ya

lullube ni naji kamar na fashe da kuka sabo da

takaici,gashi nasaa wahalar dauko ta daga cikin

wannan ramin mai zurfi har ma tafin hannuwana

sun

dade saboda kama igiya,cikin sanyin jiki na mike

na

sunkuya da nufin gawar na fita da ita waje

inda zan binne ta,kawai sai naji tayi

tari,numfashint

a

ya dawo,nan take murna ta kamani na ruga na

dauko

wani ruwan magani na dura mata a baki dakyar

tasha

mukurwa uku,jin kadan sai idanunta suka bude

dakyar,koda tayi arba dani sai naga ta firgita ta

yunkura zata tashi amma sai na danne kafadunta

na

hana ta tashi,matar ta budi baki da nufin tayi

magana

sai ta kasa,kawai sai naga tana dariya,wani

lokacin

kuma sai ta hade fuska ta kama kuka tana fisge-

fisge,nan fa na gane lallai wannan mata ta samu

tabin

hankali,al'amarin da yayi matukar bakanta raina

kenan domin naso ace ta iya yin magana acikin

hankalinta,domin na tambayeta ko ita wacece da

kuma wadannan mutane da suka kawo ta dajin

acikin

keken doki a matsayin gawa,abinda zuciyata ta

aiyana

min shine in ma basu bane to sun san wanda ya

kasheta,kuma akwai wani boyayyen al'amari akan

kisan nata,daga wannan rana naci gaba da jinyar

wannan mata har tsawon kwana ashirin da

daya,A

tsawon wadannan kwanaki kullum a kwance take

kuma koda tayi yunkurin mikewa zaune sai ta

kasa

sabo da raunin da yake makogwaronta,haka

kuma

bata taba yin magana ba sai fisge-fisge da dariya

irinta mahaukata,abinci kuwa sai dai na dura

mata

abaki tana ci tana kuka sabo da ciwo,da yake

naga

tana dauke da juna biyu sai na dinga yawan bata

madarar shanu gami da abincin da yake gina jiki

domin abinda ke cikinta ya samu cikakkiyar

lafiya,a

kwana a tashi har wannan mata ta shafe wata

uku cur

a wajena,a sannan ne raunin makogwaronta ya

warke sumul har ya zamana cewa tana iya

magana

sosai,amma a koda yaushe babu magana ta

hankali

da nutsuwa a tare da ita sai maganganu irin na

mahaukata,nayi iya kokarina akan ta gayamin ko

ita

wacece,daga inda take da kuma yadda akayi ta

shiga

wannan hali sai tayi ta kyalkyala mini

dariya,ganin

hakane yasa tausayinta ya karu a zuciyata,sau

bakwai

ina nemo masana ilimin maganin

mahaukata,wato

likitocin mahaukata suna zuwa su dubata kuma

su

bata magani,amma duk a banza lafiya taki

samuwa,sau tari matar takan sulale ta nausa

cikin

daji bansani ba,sai nasha wahalar nemota,bisa

wannan dalilin ne ma duk sanda zan fita kiwo ko

farauta sai na tafi tare da ita,wato na daina

barinta a

gida.

Lokacin da cikinta ya tsufa sai tafiya da ita kiwo

ko

farauta ya gagara,don haka nima sai na hakura

da

zuwa ko ina,na tanadi abincina da na dabbobi na

mai

yawa wanda zai kai tsawon kwana arba in,Ai

kuwa

adaren kwana lo talatin da bakwai nakuda ta

kama

wannan mata acikin tsakiyar dare.Al'amarin da

yai

matukar dugunzuma hankalina kenan tunda babu

halin in ruga cikin gari in nemo ungozoma,Da

yake na

taba shiga irin wannan hali da nake tare da

matata

wacce ta rasu a wajen haihuwa abinda ta haifa

ma

yazo a mace,sai na shiga taimakon wannan

mata,nine

na yankewa jaririn cibiya,na wanke shi sannan na

kimtsa mahaifiyar tasa,matar taci gaba da rainon

jaririnta tana shayar dashi ni kuma ina cigaba da

fita

farauta da kiwona ina barinsu a gida,har tsawon

shekara daya da wata bakwai muna tare sannan

yaron ya fara tafiya da kafafunsa.

Kwatsam wata rana naje kiwo na dawo sai na

nemi

wannan mata sama da kasa na rasa,kuma ga

dannan

ta bar shi acikin bukka a zaune shi kadai yana ta

tsala

kuka,cikin dimaucewa na dauki yaron na gaya shi

a

bayana sannan na bazama neman wannan mata

wacce ko sunanta ban saniba bare na dinga

kwalla

mata kira,Abu kamar wasa sai da na shekara

daya da

wata tara ina nemanta amma ko alamunta ban

gani

ba acikin wannan daji.A tsawon wannan lokacin

ni

nake kula da wannan yaro da ta haifa dare da

rana,ya

zama cewa na shaku dashi ainun shima haka

.Kwatsam wata rana da yammaci ina wasa da

yaron a

kofar bukkata kawai sai na hango wannan mata

daga

can nesa ta durfafo bukkata,cikin alamun

tsananin

mamaki na mike tsaye na zuba mata idanu,matar

ta

rame matuka,kuma duk rigar jikinta ta

yayyage,sannan tayi baki sabo da wahala da

kazanta,koda ta iso daf dani ta dubeni sai ta

fashe da

kuka ta durkusa kasa bisa gwiwoyinta tana mai

neman gafarata tamkar mai cikakken hankali,nan

take

naji na kamu da tsananin tausayinta don haka sai

na

kama kafadunta na tasheta tsaye kuma na

rungumeta

a kirjina a karon farko tun haduwa ta da ita,ita

kuma

sai ta kankame ni ta da da fashewa da

kuka,kawai sai

na janye jikina daga nata na dubeta nace me

yasa

kika gudu kika barmu?shin kin manta ne cewa

kin bar

danki a hannu na?koda jin haka sai matar ta dubi

dan

nata ta girgiza kai tace ai ni kananin yaro na bar

maka

bai kai wanan girma ba,da jin haka sai nayi

dariya

nace to ai kullum mutum dada girma yake har

yanzu

baki gaya min inda kika tafi ba kika barmu,Matar

ta

bushe da dariya sannan ta hade fuska tace shan

iska

na tafi na sake dawowa.Cikin tsananin damuwa

nace

yau shekara hudu kenan muna tare baki taba

gaya

min sunanki ba kuma baki gaya min sunan

garinku ba

bare nasan asalinki da danginki shin bakya

tausayin

wannan yaron da kika haifa ne?Koda jin wannan

tambaya sai matar ta sake bushewa da dariya

tace

bansan kaina ba kuma bansan kowa ba sai

kai,tana

gama fadin haka ta juya ta shige cikin bukka taje

ta

kwanta ta kama bacci,tun daga wannan rana

muka ci

gaba da zama tare,amma ko kadan wannan da

nata

bai dameta ba,kuma bata yi masa komai sai dai

ni

nayi masa,wani lokaci sai naga kamar hankalinta

ya

dawo tana magana a nutse,amma da zarar na

fara

tambayarta asalinta da garinsu sai ta birkice ta

koma

hauka.

Wata biyu da kwana uku mukayi tare ranar

kwana na

ukun ne matar ta wayi gari da tsananin rashin

lafiya

wadda bansan sanadinta ba,cikin rudewa na

shiga

hada mata magunguna iri-iri ina bata tana sha

amma

duk a banza tamkar kara mata ciwon akeyi,kawai

sai

naga idanunta sun fara lumshewa kuma

numfashinta

na sarkewa,Al amarin da ya dugunzuma

hankalina

kenan na fara zubar da hawaye,na shiga yi mata

tambayoyi akan ta sanar dani asalinta,matar na

kokarin bude baki tayi magana amma sai ta

kasa,nan

take jikinta ya sandare,idanunta suka kafe ta

daina

motsi.koda naga haka sai na rungumeta na fara

kuka,ganin ina kuka ne dannata wannan yaro dan

shekara kusan hudu ya rugo izuwa kaina shima

ya

fashe da kuka.Hakika wanan rana nayi kuka mai

yawa

sabo da shakuwar da nayi da matar nan sai da

nayi

kwana ashirin da daya bana iya cin abinci

sosai,amma koda yaushe hankalina yana kan

wannan

yaron ina kula da lafiyarsa sosai.

Koda tsoho Imzanu yazo nan a zancensa sai

Imhal ya

tari numfashinsa suka dubi juna a lokacin da

kowannensu yake zubar da hawaye yace yakai

Abbana na gane cewa wannan yaro da

mahaukaciya

ta haifa ba wani bane face ni dinnan,tabbas

yanzu na

tabbatar da cewa ni marayane wanda bashi da

uwa

bashi da uba kuma wanda baisan asalinsa

ba,koda

Imhal yazo nan zancensa sai tsoho Imzanu ya

rungumesa suka fashe da kuka tare,can sai

Imhal ya

janye jikinsa suka fuskanci juna ya dubi Imzanu

yace

Bazan taba yarda bani d uba ba amma ni kai na

sani

a matsayin ubana,ina son nayi maka wata

tambaya

guda daya menene dalilin da yasa kake kirana da

suna IMHAL?

.

WASA FARIN GIRKI


____ shin acigaba ko Kuma?

Comments

Popular posts from this blog