Rijiya gaba dubu part 2


 RIJIYA GABA DUBU

littafi na daya

  Part 2


By Yusuff smart


________

Koda jin wannan tambaya sai hawaye ya zubowa

tsoho Imzanu yace Abinda yasa nasa maka suna

Imhal shine a iya zama na da mahaifiyarka har ta

mutu ban taba jin ta ambaci sunan wani mahaluki ba

face IMHAL,A kullum duk sanda za taci abinci sai naji

tana kiran sunansa tana cewa yazo suci abincin

tare,abinda na fahimta shine,koma wanene wannan

Imhal din lallai ya kasance babban masoyi a

gareta,zai iya kasancewa mijinta ne ko dan uwanta ne

ko mahaifinta,Abu na biyu da nake zargi shine,duk

yadda akayi mahaifiyarka ta fito daga babban gida

domin a ranar da na tsince ta acikin wannan katon

ramin mai zurfi sutturar dake jikinta mai matukar

tsada ce,babu mai sanya irinta face sarakai da

manyan attajirai,babban bakin cikina shine babu

wata shaida a tare da mahaifiyarka wadda zata iya

sawa a gano asalinta,koda tsoho Imzanu yazo nan a

zancensa sai suka sake rungume juna,daga can sai

Imhal ya dubi tsoho Imzanu yace,Lallai zan rike

sunana a zuciyata da bakina,lallai wata rana wannan

suna zai taimakeni na gano asalina.

Tun daga wannan rana Imhal da tsoho Imzanu suka

cigaba da rayuwarsu acikin daji kamar yadda suka

saba,amma sai ya zamana cewa kullum sai Imhal ya

shiga cikin garin Kisra kuma duk inda yaje si ya

tambayi mai suna Imhal,idan aka tambayeshi wane

Imhal yake nema sai ya kasa bayani domin baisan

wata inkiya ba ta Imhal din da yake nema,hakane

yasa suka dinga yiwa Imhal dariya suna cewa dashi

Bagidaje mutumin daji,saboda ganin yanayin

shigarsa ta makiyaya.

Wata rana Imhal yazo giftawa ta kofar gidan sarkin

kisra akayi sa a kuwa a lokacin sarki ya fito daga cikin

gidan sarautar zai fita rangadi kwatsam sai yayi arba

da sarki,Abinka da wanda baisan yadda ka idar

sarauta take ba sai kawai ya kurawa sarki

idanu,maimakon ya zube kasa gabansa ya kwashi

gaisuwa,ai kuwa sai dakarun sarki suka afkawa Imhal

da duka har suka kai shi kasa,cikin fushi ya yunkura

ya watsar dasu duka duk da cewar sunkai su

ashirin,nan take shima ya rufesu da duka,duk wanda

yayi wa naushi daya sai ya baje a kasa

sumamme,koda ganin haka sai ragowar dakarun

sarki suka zare takubbansu sukayi caa akan Imhal

zasu sassara shi,amma sai sarki ya daka musu tsawa

suka saurara,nan take sarkin kisra ya sauko daga kan

dokinsa yazo daf da Imhal yadda har suna iya jin

numfashin juna,sannan ya dubeshi cikin murmushi

yace,A duniya babu abinda yake birgeni sama da

jarumtaka,tabbas na yarda kai jarumi ne amma ina

son na gwada jarumtaka ta akan taka,nasan baka san

koni waye ba to nine Sarkin garin nan,koda jin haka


sai Imhal ya zube kasa bisa gwiwoyinsa yana mai

sunkui da kansa kasa yace ka gafarceni ya

shugabana,kasan cewa ni rayuwata gaba daya cikin

daji nayi ta,sau daya a sati muke shigowa cikin

garinnan,yau ne ranar farko da na fara ganinka a

rayuwata,ya shugabana kayi min afuwa domin bazan

iya fada da kai ba,Koda jin wannan batun sai sarki ya

bushe da dariya ,lokaci guda kuma ya hade rai ya

dubi Imhal cikin nutsuwa yace,ya kai wannan saurayi

ma abocin jarumtaka kayi sani cewa nahiyar nan

gaba daya babu wani jarumi ko mayaki mai karfi da

iya yaki kamata,yau shekara talatin kenan ina

gwagwarmaya da gumurzu kuma sau arba in da uku

ina lashe GASAR JARUMTAKA a kasashe arba in da

uku dake cikin wannan nahiya tamu ko sau daya ba a

taba samun jarumin da ya lakuci jikina ba bare ya

kaini kasa,naga jarumtakar jarumai da yawa a

rayuwata,amma ban taba ganin jarumi mai zafin

nama da karfin naushi kamarka ba,ina da tabbacin

cewa idan muka fafata sai na sami nasara akan ka

duk da cewar na yaba da karfinka,ka sani cewa kana

da zabi guda biyu kodai ka yakeni ko kuma yanzun

nan nasa tagobi na sare maka kai,koda jin wannan

batu sai hankalin Imhal ya dugunzuma ya mike tsaye

cikin sanyin jiki,abu na farko da ya fado masa a rai

shine,Ai bai kamata ya mutu yanzu ba har sai ya gano

asalinsa,koda gama aiyana hakan acikin zuciyarsa sai

ya mikawa wani badakare hannu yace bani

tagobinka,ba tare da gardama ba kuwa ya mikawa

Imhal tagobinsa ya karba,koda ganin haka sai murna

ta kama sarki,shima ya zare tagobinsa,a lokacinne

dakaru suka buda suka yi musu da ira aka sa su a

tsakiya,nan fa sarki da Imhal suka fara zagaya juna

suna kallo-kallo.

Lokaci guda kowannensu ya daga tagobinsa sama

suka ruga izuwa kan juna,suka ruguntsume da

azababben yaki ya zamana suna kaiwa juna sara da

suka cikin tsananin zafin nama,juriya da bajinta ta

ban al'ajabi,sai da suka shafe sa a guda suna wannan

bakin artabun amma dayansu bai samu nasarar koda

kwarzanar mutum daya ba,Al'amarin da ya fusata

sarki kenan kuma ya cika da tsananin mamakin yadda

akayi wannan mutumin dajin ya samu gagarumin

horon yaki haka,nan take sarki ya canza salon yaki,ya

dinga tsalle-tsalle da kwance-kwance,kawai sai yaga

Imhal ya iya duk irin abinda yake yi tamkar tare aka

koya musu yaki babu wani banbanci,koda ganin haka

sai sarki ya ja da baya taku biyar,shima Imhal sai yayi

hakan amma shi taku uku yayi,duk su biyun suka

kurawa juna idanu na tsawon yan dakiku kadan,kawai

sai sarki ya rugo da gudu izuwa kansa,shima sai ya

ruga gareshi,kafin su hadu sai kowannensu ya daka


wawan tsalle sama ya kai hari cikin mugun nufi,Acikin

tsananin zafin nama kowannensu ya kaucewa harin

takubbansu suka sari iska,amma kafin su duro kasa

sun gwarawa juna fuska,ai kuwa sai hancin

kowannensu ya fashe,a saman sai suka sake kaiwa

juna hari,sai sarki ya sami nasarar yankar Imhal a

saman cibiyarsa,Shi kuma ya sami nasarar yankar

sarki a gefen wuyansa,kowannensu jini yayi tsartuwa

daga jikinsa suka rikito kasa a matukar galabaice,A

guje Dakaru suka ruga aka baiwa Sarki rawani ya

daure wuyansa da jini,take likitan Sarki yayi masa

magani,Kawai sai Dakaru suka ruga izuwa kan Imhal

wanda yake kwance a kasa ya dafe raunin don tsaida

jini zasu halaka shi,Sarki ya daka musu tsawa suka

fasa,kawai sai sarki ya dubi likitansa yace Idan ka

gama dani kaje kayiwa wannan saurayin magani,Cikin

gaggawa kuwa likita ya gama yiwa sarki magani

sannan yaje yayiwa Imhal,Sa ar da Sarki da Imhal

sukayi raunikan basuyi zurfi ba a jikin su,Tunda

Likitan ya fara yiwa sarki magani sai zuciyar Sarki ta

fara tafarfasa kamar zata kone saboda tsananin bakin

ciki da takaici bisa ganin yadda a yau wannan bakon

saurayi ya karya alkadarinsa na jarumin dake rike da

KAMBUN JARUMTAKA na nahiyar gaba daya,Bayan

angama yiwa Imhal magani ya mike tsaye sai yazo

gaban Sarki ya risina yayi godiya,Sarki ya dube shi

cikin yake yace Tabbas ka cika jarumi abin kwatance

amma ka saurari ranar da zamu sake haduwa a filin

gasar JARUMTAKA wacce za ayi a birnin MISIRA nan

da cikar wata uku,ko kana so ko baka so sai ka shiga

wannan gasa kuma ina tabbatar maka da cewar sai

na sami nasara akan ka na kasheka murus har

Lahira,yin hakane kadai zai sa na huce bisa takaici da

bakin cikin da ka jefani a ciki,Koda ya gama fadin

hakan sai Sarkin Kisra ya dubi wani babban Badakare

nasa yayi masa rada a kunne sannan ya juya ya kama

dokinsa ya hau ya kada linzaminsa yayi gaba,sauran

dakarun gaba daya suka rufa masa baya.Shi kuwa

jarumi Imhal sai ya tsaya cak yabi sarkin kisra da

kallo cikin tsananin mamaki,Imhal ya tambayi kansa

cikin zuciyarsa yace WAI SHIN MENENE YAYI ZAFI

HAKA,HAR DA SARKI YACE ZAI KASHENI MURUS HAR

LAHIRA ALHALIN MA BASU TABA GANIN JUNA BA

SAI YAU?AKAN WANE DALILI ZAI TSANANTA GABA A

TSAKANINMU HAKA?


Kukasance damu a part 3

In Allah ya kaimu .....


#YusuffSmært

Comments

Popular posts from this blog